LABARAI/NEWS

Buhari ya sanar da hanyar da yake so a bi wurin zaban ɗan takarar shugaban ƙasa na APC

Buhari ya sanar da hanyar da yake so a bi wurin zaban ɗan takarar shugaban ƙasa na APC

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari bayan ganawa da gwamnonin jihohin APC, ya bayyana cewa zaɓen fidda ɗan takaran shugaban ƙasa na jam’iyyar APC za’a gudanar da shi ne bisa tsarin wakilan jam’iyya “delegate” ba maslaha ba wato “Consensus”.

Tuni dai jamiyyar APC ta ƙasa ta fitar da adadin wakilai “delegates” da za su yi zaben ɗan takarar Shugaban ƙasa a ko wanne yanki a faɗin Najeriya.

1- Kudu maso Gabas — 288
2- Kudu maso Yamma — 411
3- Kudu maso Kudu — 359
4- Arewa maso Yamma — 558
5- Arewa ta Tsakiya — 363
6- Arewa maso Gabas — 336

Arewacin Najeriya — 1,257
Kudancin Najeriya — 1,068

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button