LABARAI/NEWS
Burkina Faso Ta Ba Sojojin Faransa Wata Ɗaya Su Fice Daga Kasarta

Burkina Faso Ta Ba Sojojin Faransa Wata Ɗaya Su Fice Daga Kasarta
Gwamnatin mulkin soja ta Burkina Faso ta bukaci dakarun kasar Faransa da su bar kasarta nan da wata daya
Matakin wanda Ma’aikatar Harkokin Wajen kasar ta sanar da dauka ranar Asabar na nuna yadda dangantaka ta yi tsami tsakanin Burkina Faso da kasar da ta taba yi mata mulkin mallaka
Dangantaka tsakanin kasashen biyu dai ta fara yin tsami ne tun bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a kasar a watan Satumbar bara
gwamnatin ta dauki matakin yi fatali da yarjejeniyar sojoji ta 2018 da ta ba dakarun na Faransa damar yin sansani a cikin kasar su
Sai dai har yanzu gwamnatin Faransar ba ta ce uffan ba a kana matakin